Yanzu-yanzu: Matsalar Karancin Man Fetur A Najeriya Zata Zo Karshe Daga Laraba – NNPCL

Kamfanin Man Fetur na Najeriya ya tabbatar wa ‘yan Najeriya cewa za a shawo kan matsalar karancin man fetur da layukan da ake fama daga ranar Laraba.

Olufemi Soneye, babban jami’in sadarwa na NNPC, ne ya tabbatar da hakan ga Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya ranar Talata a Legas.

Soneye ya bayyana cewa a halin yanzu kamfanin ya mallaki sama da lita biliyan 1.5 na kayayyakin, wanda ya isa na akalla kwanaki 30.

Scroll to Top